Nigeria: Boko Haram Ta Kashe Mutane 12 A Borno

‘Yan kungiyar ta boko haram sun kashe masu sintiri farafen hula 2 da kuma wasu sana’ar yin sarar itace  su 10 a  a Bokko Gjide

‘Yan kungiyar ta boko haram sun kashe masu sintiri farafen hula 2 da kuma wasu sana’ar yin sarar itace  su 10 a  a Bokko Gjide a karamar hukumar Gwoza dake Jahar Borno. Sarkin Gwoza Alhaji Muhammad Shehu Timta ya tabbatar da kisan mutanen da aka fi kira da (Civilian JTF) bayan da aka yi musu kwanton bauna a kan hanyar Kirawa.

Haka nan kuma ya kara da cewa; mutanen sun shiga cikin daji ne domin saro itace, a ranar Asabar, a yayin da masu dauke da makaman su ka yi musu kwanton bauna su ka kashe kashe daga cikinsu, sannan kuma su ka yi wa wasu biyu munanan raunuka.

Sarkin ya kara da cewa; Mun yi jana’izar 10 daga cikinsu sannan kuma mu ka dauke wadanda su ka jikkata zuwa Maiduguri domin samun magani.

Wannan harin na Boko Haram ya afku ne bayan sa’o’i 48 da shugaban kasar Bola Ahmad Tinubu ya aike da ministan tsaro Badaru Abubakar, da kuma babban jami’in tsaro na soja Janar Christopher Musa, domin su yi bitar halin tsaro da ake ciki a Jahar ta Borno.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments