MDD Ta Kira Yi Isra’ila Da Dakatar Da Hare-haren Da Take Kai Wa Syria

Babban magatakardar MDD Antonio Gutrres ya kira yi HKI da ta dakatar da hare-haren da take kai wa Syria da hakan yake a matsayin keta

Babban magatakardar MDD Antonio Gutrres ya kira yi HKI da ta dakatar da hare-haren da take kai wa Syria da hakan yake a matsayin keta hurumin wannan kasa.

Babban magatakardar MDD ya bukaci ganin Isra’ilan ta yi aiki da tsagaita wutar yaki da aka yi a 1974 a tsakaninta da Syria.

A gefe daya babban magatakardar MDD ya yi ishara da halin da ake ciki a kasar ta Syria da mutane suke da bukatuwa da kayan agaji, tare da cewa a yanzu sun mayar da hankalinsu akan wannan batu.

Har ila yau babban magatakardar  MDD ya ayyana wata lauya ‘yar kasar Mexico Karl Quintana a matsayin wacce za ya kula da batun gano wadanda su ka bace a kasar Syria. Gutrres ya kuma bukaci ganin an bai wa Quintana damar shiga kowane lungo da sake a cikin kasar ta Syria domin gudanar da aikinsu.

Tun bayan da masu dauke da makamai su ka kawo karshen gwamnatin Basshar Asad ne a ranar 27 ga watan Nuwamba na wannan shekarar mai karewa, HKI take  kai wa Syria hare-hare da kuma mamaye wasu yankunan mabanbanta na kasar da su ka hada da tuddan Gulan.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments