Kwamitin tsaro na MDD ya kada kuri’ar amincewa da sabuwar rundunar da kungiyar tarayyar Afirka ta akie zuwa kasar Somaliya, wacce za ta maye gurbin tsohuwar rundunar mai suna: ( ATMIS), da sabuwar za ta dauki sunan: (AUSSOM). Wannan matakin dai yana a matsayin wani mataki ne wanda zai kai ga bai wa jami’an tsaron kasar ta Somaliya damar daukar nauyin kula da harkokin tsaron kasarsu anan gaba.
Kwamitin tsaron ya kuma yarda akan cewa kungiyar ta Afirka ta dauki dukkanin matakan da su ka dace domin a tsawon watanni 12 a matsayin ayyukan share fage na tabbatar da tsaro. Ayyukan na sabuwar rundunar za su fara ne daga ranar 1 ga watan Janairu na 2025 da za a shiga, sun kuma kunshi taimakawa gwmanatin tarayyar Somaliyan a fada da kungiyar al-shabab, da kuma sauran kungiyoyi masu alaka da D’aesh.