Kasar Masar ta sanar da tattaunawa da Amurka kan batun shirya sake gina zirin Gaza bayan yakin kisan kare dangi na shekaru biyu da Isra’ila ta kaddamar kan yankin.
“Yanayin da ke faruwa a Yammacin Kogin Jordan bai yi muni kamar na Gaza ba,” in ji Ministan Harkokin Wajen Masar Badr Abdelatty a wani taron manema labarai na hadin gwiwa da takwaransa na Jamus.
M. Abdelatty ya sanar da cewa Alkahira tana tattaunawa da Amurka game da wani taron kasa da kasa da nufin sake gina yankin Gaza, bayan yakin.
A wani taron manema labarai na hadin gwiwa a Berlin ranar Talata da takwaransa na Jamus, Johann Wadephul, Abdelatty ya nuna cewa ana ci gaba da tattaunawa da Washington don sanya ranar taron, wanda Masar da Amurka za su jagoranci tare.
Yakin kisan kare dangin da Isra’ila ta kwashe shakaru biyu tana yi a Gaza ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 70.000 a zirin galibi mata da kuma yara.