Wata majiya ta hizbbulla ta fadawa gidan talabijin din al-hadatha cewa kungiyar tana nan kan bakanta na yarjejeniyar dakatar da bude wuta da aka sanyawa hannu tsakaninta da isra’ila musamman a yankunan kudancin kasar da kuma tekun litani
Duk da yarjejeniyar dakatar da bude wuta da aka cimma a watan decembar shekara ta 2024 amma akwai fargaba sosai a iyakokin labanon da Isra’ila , sai dai hizbullah ta fitar da sanarwa a baya bayan nan wanda ke nuna shirinta na mayar da martani mai tsanani idan israila ta tsokaneta, duk da kasashen yamma na kokarin ganin an kawar da makamai da kuma rage tasirinsu, adaidai lokacin da ake ci gaba da nuna damuwa kan yiyuwar sake barkewar wani rikici
Ministan harkokin wajen kasar faransa Jean-neol barrot ya bayyana cewa kasarsa na goyon bayan kwabe makaman hizbullah kuma yayi kira ga isra’ila da ta janye daga wurare biyar masu muhimmanci a kudancin labanon.