Iran Da Qatar Sun Tattauna Kan Dangantakar Dake Tsakaninsu

Rahotanni sun bayyana cewa ministan harkokin wajen kasar iran ya tattaunawa da takwaransa na kasar Qatar kan dakangantar dake tsakaninsu da kuma abubuwan da ke

Rahotanni sun bayyana cewa ministan harkokin wajen kasar iran ya tattaunawa da takwaransa na kasar Qatar kan dakangantar dake tsakaninsu da kuma abubuwan da ke faruwa a yankin, inda dukkan bangarorin biyu suka yi kira kan muhimmancin yin aiki tare adaidai lokacin da ake cikin wani yanayin a kudu da yammacin Asia.

Wannan tattaunawar tana nuna irin yadda kasashen biyu suke son ganin sun kara karfafa huldar diplomasiya da tattalin arziki a bangarorin daban- daban kuma sun nuna damuwa game da yadda rikici ke kara Kamari tsakanin kasashen Pakistan da Afghanistan, don haka sun jaddada game da muhimmacin tabbatar zaman lafiya a yankin baki daya,

Ministocin harkokin wajen sun tabo batun  ci gaba da aka samu a baya bayan nan a yankin Gaza, inda suka yi kira da a hada kai a ci gaba da nuna goyon bayan Alummar falasdinu . Wannan yana zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa kan alamuran gaza, manufofin Amurka da makomar yancin kai na falasdinu, inda ake ganin kasashen biyu a matsayin masu ruwa da tsaki wajen tsara zaman lafiya da tsaro a yankin.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments