Kasar Iran ta bayyana sake kulluwar hulda da Amurka ta hanyar masu shiga Tsakani
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin siyasa Majid Takht-Ravanchi ya sanar da cewa: Wasu kasashe na tuntubar Iran da Amurka a matsayin masu shiga tsakani.
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin siyasa ya shaidawa tashar Haber Turk ta Turkiyya cewa: Akwai tuntuba tsakanin Iran da Amurka ta wasu kasashe masu shiga tsakani, yana mai cewa: “Wasu kasashe suna hulda da Iran da Amurka, kamar yadda kuka sani, don haka Iran tana tattaunawa da Oman a matsayin mai shiga tsakani.”
Da yake amsa tambaya game da ganawar da kungiyar Tarayyar Turai a Istanbul, ya ce: “Iran ta sake gudanar da wani zagaye na shawarwari tare da kasashen Turai a matakin mataimakan ministoci. An dade ana ci gaba da gudanar da wannan tsari, tana ganawa da tattaunawa kan batutuwa daban-daban kan batun makamashin nukiliya. A taron jiya sun tattauna batutuwan fasaha na batun makamashin nukiliya da kuma batun dage takunkumin da aka sanyawa kasar Iran, kamar yadda Iran din ta jaddada cewa dole ne a samar da duk wani bangare na inganta sinadarin Uranium a cikin kasar Iran.”