Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana cewa addinin musulunci ya daukaka matsayin macce ya kuma bada matsayin guda da maza a fagagen zamantakewa da siyasa, ya kuma yi watsi ya akidar kasashen yamma wadanda suka kaskasntata suka maida ita kayan aika don cimma bukatatun wasu.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jagoran yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar a taron dubban mata daga yankunan daban daban na kasar a yau laraba a nan Tehran.
Imam Khaminae ya ce, mata a Iran suna koikoyon Fatimah Azzahra (s) diyar manzon Allah (s) don haka suka kama hanyar daukaka wanda alah ya bawa mata. Fatima (s) makaranta ce ga mata kuma daukaka ce a garesu.
Imam Khaminae ya ce aladun kasashen yamma da kuma tsarin jarin hujja dangane da mata ba amintaccene a addinin musulunci ba. Yace tsare-tsaren da addinin musulunci ya zo da su na, hijabi da hana cakudar mata da maza a tarurruka, da kudaitar da aure da sauransu duk don kare Martaban mata ne a mataki na farko. Yace musulunci bai hana mata shiga a dama da su a cikin al-amuran zamantake da siyasa da sauransu ba, amma tare da kiyaye mutuncinta, da aikita na asali wanda shi ne kula da iyala da tarbiyyan yayanta.