Isra’ila Ta Kai Sabbin hare-hare 60 Kan Siriya

Isra’ila ta sake kai wasu sabbin hare-hare a kasar Siriya, wadanda su ne na baya bayan nan data kai tun bayan faduwar gwamnatin Bashar Al-Assad.

Isra’ila ta sake kai wasu sabbin hare-hare a kasar Siriya, wadanda su ne na baya bayan nan data kai tun bayan faduwar gwamnatin Bashar Al-Assad.

Tun bayan lamarin Isra’ila ta fara kai hare-hare kan wurare da daman a Siriya musamman cibiyoyin soji da wuraren adana makamai.

Sama da hare-hare 60 Isra’ila ta kai a cikin ‘yan sa’o’i kadan kan wuraren soji a fadin kasar ta Syria, a baya baya nan kusan mako guda bayan kwace Damascus daga hannun gwamnatin Bashar al-Assad, in ji wata kungiya mai zaman kanta.

Kungiyar kare hakkin bil adama ta kasar Syria (SOHR) ta sanar da cewa, “An kai hare-hare 61 cikin kasa da sa’o’i biyar” da yammacin ranar Asabar da Isra’ila ta yi.

Kungiyar ta kara da cewa: “Isra’ila na ci gaba da zafafa hare-hare ta sama kan yankunan kasar Siriya.

Hare-haren da Isra’ila ta kai Siriya sun kai “446 tun bayan faduwar gwamnatin Bashar al-Assad.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments