Isra’ila Na Ci Gaba Da Kai Munanan Hare-hare Kan Siriya

Isra’ila na ci gaba da kai munanan hare-hare kan yankuna daban-daban a fadin kasar ta Siriya, yayin da mayakan da ke samun goyon bayan kasashen

Isra’ila na ci gaba da kai munanan hare-hare kan yankuna daban-daban a fadin kasar ta Siriya, yayin da mayakan da ke samun goyon bayan kasashen yammacin duniya, wadanda suka hambarar da gwamnatin kasar a farkon wannan wata, suka karfafa musu gwiwa.

A ranar Litinin, jiragen yakin Isra’ila sun kai hari kan muhimman wurare da kayayyakin aikin soji a gabar tekun yammacin kasar, ciki har da biranen Tartus da Latakia, inda suka yi luguden wuta kan sansanonin makamai masu linzami da ma’ajiyar harsasai.

An samu tashin bama-bamai masu yawa a garuruwan a lokacin hare-haren.

Tashar talabijin ta al-Mayadeen ta kasar Labanon ta ce sojojin mamaya na Isra’ila sun kuma kai hari a wani yanki mai nisan kilomita 15 a lardin Quneitra na yammacin kasar Siriya.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya kuma bayar da rahoton hare-haren da Isra’ila ta kai kan cibiyoyin soji a Hama da Homs, wasu larduna biyu na yammacin kasar, inda ya kara da cewa hare-haren da aka kai kan Hama da Aleppo, wadanda ke a yammacin Syria, sun girgiza wuraren da aka kai harin kamar girgizar kasa.

A bangare guda, majiyoyin cikin gida sun bayar da rahoton cewa, jiragen yakin gwamnatin kasar sun kuma kai hari a filin jirgin saman soji da ke lardin Deir al-Zawr da ke gabashin kasar.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments