Iran : Zamu fifita diflomasiyya da kasashe makwabtanmu

Iran ta ce za ta fifita diflomatisyya ta tsakaninta da kasashe makobtanta na yankin. Ministan harkokin wajen kasar ne Abbas Araghchi ya jaddada aniyar kasar

Iran ta ce za ta fifita diflomatisyya ta tsakaninta da kasashe makobtanta na yankin.

Ministan harkokin wajen kasar ne Abbas Araghchi ya jaddada aniyar kasar kan harkokin diflomasiyya a yankin, yana mai bayyana cewa kasashen da ke makwabtaka da kasar na cikin tsarin Jamhuriyar Musulunci.

“Makwabtanmu sune fifikonmu,” in ji ministan harkokin wajen Iran a cikin wani sako da aka wallafa a shafinsa na X.

Mista Araghchi ya tattauna da takwarsana na Omani, Badr bin Hamad Al Busaidi, a Muscat, babban birnin kasar Omani, inda suka tattauna muhimman batutuwan da suka shafi kasashen biyu da na shiyya-shiyya.

Babban burinmu shi ne kare zaman lafiya da kwanciyar hankali ta hanyar diflomasiyya.

Ziyarar ta Araghchi a birnin Muscat na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin yankin ke ci gaba da ruruwa, sakamakon kisan kiyashin da gwamnatin Isra’ila tare da goyon bayan Amurka ke aiwatarwa a zirin Gaza da kuma yadda ake ci gaba da kai munanan hare-hare a wasu wurare a yankin musamman a Syria da Lebanon.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments