Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi Allah wadai da hare-haren da aka kai wa fararen hula a Sudan
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana damuwa game da rikicin makamai da ya barke a El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Sudan, yana mai Allah wadai da lalata kayayyakin more rayuwa da kuma kisan fararen hula marasa laifi a birnin.
A cewar wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta fitar a yammacin jiya Talata, Baqa’i ya nuna damuwa game da rikicin makamai da ya barke a El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Sudan, yana mai Allah wadai da lalata kayayyakin more rayuwa da kuma kisan fararen hula marasa laifi a birnin.
Baqa’i ya yi gargadi game da daukar matakai masu hatsari da nufin kara raba Sudan, yana mai jaddada bukatar girmama ikon mallakar kasa da kuma cikakken yankin kasar Sudan.