HKI Ta Kai Hare-hare A Falasdinu Da Kasar Lebanon

Sojojin mamayar HKI sun kai sabbin hare-hare a wasu yankuna na gabashin kasar Lebanon, adaidai lokacin da take ci gaba da kai wa yankin yammacin

Sojojin mamayar HKI sun kai sabbin hare-hare a wasu yankuna na gabashin kasar Lebanon, adaidai lokacin da take ci gaba da kai wa yankin yammacin kogin Jordan wasu gare-haren.

Kafafen watsa labarun HKI sun ambaci cewa; Sojojin mamayar sun kame Falasdinawa 5 a garin al-Khalil dake kudancin yammacin kogin Jordan. Haka nan kuma sun kama wasu Falasdinawa 8 a garin Nablus.

A garin Bireh da wasu yankuna na Ramallah, sojojin mamayar sun kai wasu hare-haren a yau Laraba.

A cikin watannin bayan nan, sojojin HKI sun rushe gidajen Falasdinwa 79 a cikin yankin yammacin kogin Jordan, tare da tilastawa mazaunan gidajen kusan 40,000 yin hijira.

A ranar 22 ga watan Maris ne dai jiragen yakin HKI su ka kai hare-hare a garuruwan Lebanon da su ka hada, Nabi Shit, Hermel, da wasu garuruwan da suke a yankin Bika. Haka nan kuma sun kai wasu hare-haren a garin Deir Qanun.

Tun daga fara yaki akan Gaza, sojojin HKI sun kashe Falasdinawan da sun haura 50,000, yayin da wani adadin da ya kai mutane113,000 su ka jikkata.

A can yankin Gaza ma, sojojin na HKI suna cigaba da kai hare-hare wanda ya yi sanadiyyar samun shahidai da dama.

Hare-haren na sojojin mamaya ya shafi garin Khan-yunus dake kudancin Gaza, haka nan kuma a garin Rafaha dake kan iyaka da kasar Masar.

Da safiyar yau Laraba kadai Falasdinawa 11 ne su ka yi shahada, daga cikinsu da akwai kananan yara 5.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments