Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Jiya Laraba

A ci gaba da tafka laifukan yakin da HKI take yi a Gaza,Fiye da Falasdinawa 60 ne su ka yi shahada a jiya Laraba. A

A ci gaba da tafka laifukan yakin da HKI take yi a Gaza,Fiye da Falasdinawa 60 ne su ka yi shahada a jiya Laraba.

A wani harin da sojojin mamayar su ka kai a yankin Jabaliya, Falasdinawa 5 sun yi shahada, yayin da wani adadi mai yawa su ka jikkata.

Wani jirgin sama maras matuki ya kai wani harin a unguwar “Shuja’iyya” wnada ya yi sanadin shahadar mutum daya, sai kuma wasu shahidan 4 a unguwar “Shari’u 5”, da kuma wasu shahidan 4 a garin “Bani-Suhaila”.

Wasu rahotannin sun ce, ‘yan sahayoniyar sun kai wasu hare-haren a garin ‘Abasan al-kabira’ da ya yi sanadin shahadar mutum daya da kuma jikkatar wasu masu yawa.

A yankin Qizan kuwa, ‘yan sahayoniyar sun kai hari akan mutanen da suke kokarin isa wurin da za su sami kayan agaji, tare da kashe 5 daga cikinsu a yankin kudu maso yammancin garin Khan-Yunus.

Ita kuwa hukumar yankin na Gaza ta sanar da cewa; ‘yan sahayoniyar sun kashe fararen hula 10 wadanda yunwa ci karfinsu, sannan kuma ta jikkata wasu 62 a wurin da aka ware na raba kayan agaji.

Sanarwar ta hukumar Gaza ta kuma ce; Yankunan da aka ware domin raba kayan agaji a karkashin Amurka da Isra’ila’ ya zama tarkon da ake kashe mutane a wurin.

A gefe daya ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa; Sojojin mamaya sun kai wa asibitin tafi da gidanka na  “Red-Cross” hari dake “Mawasi, a gundunar Khan-Yunus. “Yan mamayar sun kai harin ne adaidai lokacin da ake yi wa wadanda su ka jikkata magani.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments