Dubban Mutanen Moroko Sun Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Bayan Falasdinawa

Dubban mutanen kasar Moroko ne su ka fito kan titunan birnin Rabat domin yin Zanga-zangar nuna goyon bayansu ga al’ummar Falasdinu da HKI take yi

Dubban mutanen kasar Moroko ne su ka fito kan titunan birnin Rabat domin yin Zanga-zangar nuna goyon bayansu ga al’ummar Falasdinu da HKI take yi wa kisan kiyashi.

Mahalarta Zanga-zangar sun hada lauyoyi, dalibai, kungiyoyin fararen hula da sauran mutanen gari, suna dauke da tutar Falasdinu, tare da kuma da bayar da taken: “Yanci ga Falasdinu, da yin kira da a shigar da kayan agaji a cikin yankin na Gaza.

Bugu da kari, masu Zanga-zangar sun yi gangami a bakin ginin majalisar dokokin kasar.

Mutanen sun nuna rashin amincewarsu da  halin da mutanen Gaza suke ciki, tare da yin kira da a kawo karshensa.

Mahalarta Zanga-zanagr dai sun fito ne daga biranen Tangier, Casbalanca da Feiz, da kuma wasu garuruwa na kasar ta Moroko.

Al’ummar Moroko dai suna cikin masu yawaita Zanga-zanga da gangami domin yin tir da kisan kiyashin da HKI take yi wa mutanen Gaza, da kuma nuna kin amincewa da halin ko’in kula na gwamnatocin kasashen larabawa.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments