Araghchi: Halayyar Amurka ce yin matsin lamba maimakon diflomasiyya a dangantaka ta kasa da kasa

Ministan Harkokin Wajen Iran ya ce: “Bayan zagaye biyar na tattaunawa, yayin da muke shirin zagaye na shida, ɓangaren Amurka ya karya hanyar diflomasiyya da

Ministan Harkokin Wajen Iran ya ce: “Bayan zagaye biyar na tattaunawa, yayin da muke shirin zagaye na shida, ɓangaren Amurka ya karya hanyar diflomasiyya da kuma ƙoƙarin shiga tsakani da ake yi.”

Seyyed Abbas Araghchi, Ministan Harkokin Wajen Iran, ya ce a wata hira da ya yi da shirin “Ma’a Musa al-Far’ei” a ranar Litinin: “Abin takaici dokokin ƙasa da ƙasa da tsarin duniya sun yi tasiri ga yanayin Amurka na amfani da ƙarfi a dangantakar ƙasa da ƙasa.”

A cewar Pars Today, Araghchi ya ƙara da cewa: “Wannan ya bayyana a cikin tsoma bakin soja na ba bisa ƙa’ida ba da kuma aiwatar da ayyukan kisan kai duk inda suka ga dama.”

Ya jaddada cewa: “Abin da muke gani a yau ya zama tushen damuwa ta duniya.”

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments