Amurka ta kai sabbin hare-hare 22 a kan Yemen

Amurka ta kai sabbin munanan hare-hare ta sama har sau 22 a wasu larduna da dama na kasar Yemen, jim kadan bayan kai wa kasar

Amurka ta kai sabbin munanan hare-hare ta sama har sau 22 a wasu larduna da dama na kasar Yemen, jim kadan bayan kai wa kasar hare-hare da dama makamancin haka.

A cewar majiyoyin na Yemen, wadannan sabbin hare-hare na Amurka sun auna yankuna daban-daban a ranar Laraba, ciki har da babban birnin kasar Sanaa da lardin Ibb da ke tsakiyar kasar.

A Sana’a, an kai hare-hare ta sama guda takwas. Har yanzu ba a tabbatar da asarar rayuka ba, amma hare-haren sun shafi muhimman ababen more rayuwa, lamarin da ke kara tabarbare yanayin rayuwa ga fararen hula.

An sami adadin wadanda suka mutu mafi muni a lardin al-Hudaydah da ke yammacin kasar, inda aka tabbatar da mutuwar fararen hula 6 da suka hada da yara biyu da mace daya.

Akalla wasu mutane 16 sun jikkata, wadanda da dama daga cikinsu na cikin mawuyacin hali.

Da wadannan hare-hare, jimillar hare-haren da Amurka ta kai kan kasar Yemen ya kai 50 cikin sa’o’i 24 kacal.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments