Albanese: Wajibi Ne A Kawo Karshen Gwamnatin Mamaya A Falasdinu

Jami’ar mai aikin tsarawa MDD rahoto akan Falasdinu  Farencesca Albanese ta bayyana cewa; tsagaita wutar yaki da aka yi a Gaza, bai wadatar ba, wajibi

Jami’ar mai aikin tsarawa MDD rahoto akan Falasdinu  Farencesca Albanese ta bayyana cewa; tsagaita wutar yaki da aka yi a Gaza, bai wadatar ba, wajibi ne a kawo karshen tsarin mamaya a Falasdinu.

Albanese ta kuma ce Amurka ce take bai wa ‘yan mamaya cikakken goyon baya a kisan kiyashin da take yi wa al’ummar Falasdinu,don haka ya zama wajibi a kawo karshen yadda ‘yan mamayar suke sarrafa albarkatun al’ummar Falasdinu,sannan kuma a tarwatsa tsarin mulkin mallaka na mamaya.

A halin da ake ciki a yanzu dai Albanese tana kasar Afirka Ta Kudu, inda take halartar taron shekara-shekara akan “Nelson Mandela” za kuma ta gabatar da jawabai a wurin.

Tun a cikin watan Mayu ne dai Amurka ta kakawa ma’aikaciyar MDD takunkumi saboda matsayarta ta sukar HKI akan laifukan yaki da kuma kisan kiyashin da take yi wa al’ummar Falasdinu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments