Zanga-zanga Ta Barke A Birnin Halab Na Kasar Syria Saboda Kama Wasu Mutane Da Sabuwar Gwamnati Ta Yi

Rahotannin da suke fitowa daga birnin Aleppo na kasar Syria sun ce da safiyar yau Lahadi mutanen birnin Aleppo sun fito a dandalin “Sa’adallah al-jabiri’

Rahotannin da suke fitowa daga birnin Aleppo na kasar Syria sun ce da safiyar yau Lahadi mutanen birnin Aleppo sun fito a dandalin “Sa’adallah al-jabiri’ domin nuna kin amincewarsu da kame wasu mutanen garin da aka yi wanda ake danganawa sabuwar gwamnati karkashin Julani.

Kungiyar Tahrir al-Sham wacce Ahmad Shar, Julani yake jagoranta ta kama wasu mata da suke neman samun ‘yanci, haka nan kuma iyalansu.

Iyalan wadanda aka kama din sun fito dauke da makamai a dandalin na birnin kasar Aleppo suna nun kin amincewa da kama ‘yan’uwansu da aka yi.

Bugu da kari masu Zanga-zangar sun bai wa shugaban gwamnatin ta Syria Julani wa’adin wasu sa’oi kadan akan ya sako musu ‘yan’uwa mata da aka kama.

Share

4 1 vote
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments