Yahudawa masu zanga-zanga a gaban ofishin Netanyahu na neman a tsagaita wuta a Gaza

Dangi da iyalan yahudawa da aka yi garkuwa da su  a Gaza sun gudanar da zanga-zanga a gaban majalisar Knesset ta Haramtacciyar Kasar Isra’ila, inda

Dangi da iyalan yahudawa da aka yi garkuwa da su  a Gaza sun gudanar da zanga-zanga a gaban majalisar Knesset ta Haramtacciyar Kasar Isra’ila, inda suka bukaci gwamnatin Netanyahu ta aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, kamar wadda aka cimma da Lebanon.

Masu zanga-zangar sun toshe kofar shiga ofishin Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da ke cikin ginin majalisar Knesset na wani dan lokaci a ranar jiya Laraba, kamar dai yadda kafafen yada labarai na Isra’ila suka ruwaito.

Masu zanga-zangar dai sun bukaci Netanyahu ya gana da su tare da cimma yarjejeniyar musayar fursunoni domin a sako mutanen da aka yi garkuwa da su a Gaza, wadanda aka kiyasta cewa adadinsu ya kai 101.

Wannan zanga-zangar na zuwa ne kwana guda bayan da majalisar ministocin Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita bude wuta tsakaninta da Lebanon.

Eli Albag, dan uwan ​​daya daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su a Gaza, ya ce kamar yadda Netanyahu ya amince da tsagaita bude wuta don dakatar da yaki da Lebanon, ya kamata ya yi hakan a Gaza.

Share

4 1 vote
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments