Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Muhammadu Buhari Ya Rasu Yana Dan Shekaru 82

A jiya Lahadi ne mai Magana da yawun shugaban kasar Najeriya, Bola Tinibu ya rubuta a shafinsa na X cewa; Shugaba Buhari ya rasu a

A jiya Lahadi ne mai Magana da yawun shugaban kasar Najeriya, Bola Tinibu ya rubuta a shafinsa na X cewa; Shugaba Buhari ya rasu a yau, a birnin London da misalin karfe 4;30″

A shekarar 2015 ne dai shugaba Buhari ya zama dan takara na farko wanda ya yi nasara akan shugaban kasar da yake kan kujerarar Mulki, Goodluck Jonatjan, a zaben da ake dauka mai inganci.

Buhari wanda janar din soja ne mai ritaya, ya Mulki Nigeria a shekaru 1980’s bayan da ya kifar da gwamnatin farar hula ta Alhaji Shehu Shagari.

A lokacin mulkinsa ya dauki matakan tsuke bakin aljihu da hakan ya jefa, mafi yawancin talakawan kasar cikin Karin talauci.

Mogoya bayansa suna daukarsa a matsayin wanda ya jagoranci fada da talauci da kuma rashin tsaro.

A lokacin mulkinsa ne a 2015 aka yi kisan kiyashin Zaria, wanda ya ci rayukan daruruwan  ‘yan kungiyar Harkar musulunci a karkashin jagorancin Sheikh Ibrahim Zakzaki

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments