Limamin Kiristocin Birnin Qudus Ya Ce: Dole Ne Duniya Ta Daukin Nauyin Da Ya Rataya A Wuyarta Kan Wahalar Gaza

Babban limamin Kiristocin birnin Qudus ya bayyana cewa: Dole ne kasashen duniya su dauki nauyin da ya rataya a wuyansu na wahalar da Falasdinawa a

Babban limamin Kiristocin birnin Qudus ya bayyana cewa: Dole ne kasashen duniya su dauki nauyin da ya rataya a wuyansu na wahalar da Falasdinawa a Gaza suke ciki

Shugaban mabiya darikar Orthodox na kasar Girka na birnin Qudus ya yi kira ga kasashen duniya da su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na magance wahalhalun da al’ummar Falasdinu suke ciki a Zirin Gaza, yana mai jaddada cewa: Tilas ne tsagaita bude wuta a matsayin matakin farko na samun zaman lafiya mai dorewa.

Shafin yada labaran Falasdinawa na “Wafa” ya watsa rahoton cewa: Shugaban darikar ta Orthodox a birnin Qudus ya kara da cewa, a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Talata, cewa: Dole ne a tsagaita bude wuta a Zirin Gaza, tare da neman samun hakikanin zaman lafiya da ke nuna adalci da kuma kiyaye mutuncin bil’adama.

Ya ci gaba da cewa: “Mummunan tasirin yakin da aka yi a Gaza bai takaita a tarwatsa kayayyakin amfanin bil-Adama ba, amma ya fadada zuwa ga samar da wani mummunan rauni mai zurfi a cikin zukatan duk mai dauke da ruhin dan Adamtaka a fadin duniya, kuma wahalar da al’ummar Gaza suka shiga tana wakiltar raɗaɗi ne a dukkanin zukatan ‘yan Adan wanda ke kira ga aikin gama gari don farfado da ka’idodin. adalci da rahama a tsakanin al’ummun duniya.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments