Lebanon: An Jikkata Sojojin Lebanon 4 A Wani Taho Mu Gama Da Masu Dauke Da Makamai Na Kasar Syria

Sojojin Lebanon sun sanar da cewa 4 daga cikinsu sun jikkata saboda fadan da ya barke a tsakaninsu da masu dauke da makamai a yankin

Sojojin Lebanon sun sanar da cewa 4 daga cikinsu sun jikkata saboda fadan da ya barke a tsakaninsu da masu dauke da makamai a yankin Ma’aribun dake Ba’alabak.

Sojojin na Lebanon sun ce da marecen jiya juma’a ne aka yi taho mu-gamar wanda ba shi ne karo na farko ba. Masu dauke da makaman daga Syria ne su ka fara kai wa sojojin na  Lebanon hari akan iyaka da hakan ya sa su ka mayar da martani.

Masu makaman na Syria, sun so bude wata hanyar shiga cikin Lebanon ne ta hanyar amfani da motar buldoza domin yin kutse cikin Lebanon. Sojojin Lebanon sun yi harbi a cikin iska domin gargadi, sai dai masu makaman sun mayar da wuta a kansu, kamar yadda sojojin na Lebanon su ka sanar.

Har yanzu babu cikakken bayani akan  dalilin da ya sa masu dauke da makaman suke yin kutse cikin kasar ta Lebanon.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments