Rahotanni sun bayyana cewa sojojin isra’ila sun kwace gidjen wasu falsdinawa a kuyen Qusra kwanaki bayan kwace kauyen dake gabar yammacin kogin Jodan, kuma sun kwace gidagen falasdinawa guda 8 a kauyen qusra a garin Nablus dake yankin falasdinu a jiya alhamis
Sojojin Isra’ila sun fara kwace yankin na Qusra ne tun a ranar lahadi inda sojojin Isra’ila da wasu yahudawa yan share wuri zauna sun kafa tenti inda suka rufe kofar shiga wasu gidaje guda 3 dake saman kauyen, kuma suna hana ruwa da wutar lantarki da kuma motar Asibiti isa wajen don daukar wani yaro mara lafiya.
Ministan harkokin wajen yankin falasdinu ya fitar da wani bayani inda yayi tir da yahudawa yan gudun hijira da suka kai hare-hare da ake bayyanashi a matsayin na ta’addanci, ya kuma ce gwamnatin tel aviv tana amfani da yan gudun hijira a matsayin kayan aiki don cimma manufofinta da kuma mamaye yammacin kogin jodan
Tun daga lokacin sojojin Isra’ila da sauran yahudawa yan share wuri zauna sun kashe falasdinawa akalla 1182 a fadin yakin gabar yammacin kogin Jodan kuma sun jikkata dubbai da kuma tilastawa mutane 24000 tserewa daga gidajensu ba shiri.