Iran Ta Kira Yi Kasashen  Mexico Da Ecuador  Da Su Warware Sabanin Dake Tsakaninsu Ta Hanyar Tattaunawa

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran  Dr. Nasir Kan’ani ya bayyana muhimmancin girmama da kare tsaron  manya da kananan ofisoshin jakadancin kasashe. Kakakin ma’aikatar harkokin wajen

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran  Dr. Nasir Kan’ani ya bayyana muhimmancin girmama da kare tsaron  manya da kananan ofisoshin jakadancin kasashe.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya kara da cewa Da akwai damuwa a tattare da rahotannin da suke nuni da cewa a birnin  Kito na kasar Ecuador an kutsa cikin ofishin jakadancin kasar Mexico.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran din  ya kuma kara da cewa; Wajibi kowace kasa ta kare hurumin ofisoshin jakadancin da suke cikinta.

Shi da Glas ya rike mukamin mataimakin shugaban kasar ne a karkashin shugaba Rafael Correa daga 2013 zuwa 2017.

Rikici a tsakanin kasashen biyu na yankin Latin ya yi kamari, ta yadda a ranar juma’ar da ta gabata, kasar Mexico ta yanke shawarar bai wa tsohon  mataimakin shugaban kasa mai ra’ayin sauyi Glas mafakar siyasa.

A ranar juma’ar da ta gabata ne dai shugaban kasar Mexico Andress manuel Lopez Orbador ya rubuta a shafinsa na x cewa; An sanar da shi cewa, ‘yan sandan Ecudor sun bayar da umaranin a kutsa cikin ofishin jakadancin domin kama Glas, wanda yake neman mafaka saboda takura masa da ake yi.”

An nuna wani hoton bidiyo da yake nuna yadda ‘yan sanda suke kai da komowa a zagayen ofishin jakadancin na Mexico.

Mexico ta sanar da yanke alakar diplomasiyya da kasar Ecudor saboda abinda ya faru.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments