Iran : Hare-haren Amurka Da Birtaniya Kan Yemen Zasu Kara Haifar Da “Rashin Tsaro A Yankin Yammacin Asiya

Iran ta yi gargadin cewa sabon harin da Amurka da Birtaniya suka kai kan kasar Yemen zai kara haifar da “rashin tsaro da rashin zaman

Iran ta yi gargadin cewa sabon harin da Amurka da Birtaniya suka kai kan kasar Yemen zai kara haifar da “rashin tsaro da rashin zaman lafiya” a yankin yammacin Asiya.

A cikin wata sanarwa da ya fitar yau Lahadi, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baghaei ya yi kakkausar suka kan hare-haren da sojojin kawancen suka kai kan ababen more rayuwa a garin Sa’ada da ke arewa maso yammacin kasar Yamen, kwanaki kadan bayan da suka yi ruwan bama-bamai ta sama a lardin Hudaidah da ke gabar tekun yammacin kasar.

Baghaei ya ce ci gaba da kai hare-haren soji da Amurka da Birtaniya da gwamnatin Isra’ila ke yi kan kasar Yaman ya zama cin zarafi a fili kan ‘yancin kan kasar ta Yemen.

Ya kara da cewa hare-haren sun sabawa ka’idoji da dokokin kasa da kasa da kuma tsarin Majalisar Dinkin Duniya.

Kamfanin dillancin labaran Saba na kasar Yemen, ya nakalto majiyar kasar da ta nemi a sakaya sunanta, ta rawaito cewa, dakarun kawancen sojojin kasashen Yamma sun kai hare-hare ta sama guda uku a gabashin birnin Sa’ada babban birnin lardin a safiyar yau Lahadi.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments