Jami’an tsaro na yansandan ciki, a kasar Yemen sun bada sanarwan lalata wani shirin hukumar liken asiri ta Amurka ;CIA; da kuma Mosad ta HKI na hargitsa al-amuran cikin kasar.
Tashar talabijin ta Al-mayadeen ta kasar Lebanon mai watsa shirye-shiryensa da harshen larabaci ya nakalto Muhammad Ali Hauthi mamba a majalisar harkokin siyasa ta kasar Yemen. Yana fadar haka ya kuma kara da cewa. Gwamnatin kasar a shirye take to fuskanci duk wani kokarin hargitsa harkokin zamantakewa da tsaron kasar ta Yemen.
Houthi ya kara da cewa sojojin kasar a shirye suke su fuskanci Amurka a duk wani kokarin da zata yi na kutsawa cikin kasar Yemen, banda haka zata sanya dukkan al-amura da suka shafi kasar Amurka gabas tatsakiya cikin hatsari. Hauthi