Gwamnatin Damascos Ta Musanta Rahotanni Da Ke Cewa Shugaba Al-Assad Ya Tsere

Ministan harkokin cikin gida na Syria ya shaidawa gidan talabijin na kasar cewa jami’an tsaro sun kafa wani shinge a kusa da Damascus yayin da

Ministan harkokin cikin gida na Syria ya shaidawa gidan talabijin na kasar cewa jami’an tsaro sun kafa wani shinge a kusa da Damascus yayin da mayakan ‘yan adawa ke cewa suna kutsawa cikin babban birnin kasar.

Mohammed al-Rahmoun ya ce “Akwai wani shingen tsaro mai karfi da sojoji sukayi wa Damascus da yankunanta, kuma babu wanda zai iya kutsawa cikin wannan layin na tsaro da sojoji sukayi,”

A wani labarin kuma ofishin shugaba Bashar al-Assad ya musanta rahotanni da ke cewa ya tsere daga Damascus, babban birnin kasar, a daidai lokacin da gungun ‘yan adawan kasar masu dauke da makamai  ke ci gaba da dannawa kan hanyar zuwa babban birnin da kuma Aleppo.

Ofishin ya yi Alla-wadai da “labaran karya da ake yada wa”, inda ya kara da cewa shugaban na ci gaba da gudanar da ayyukansa daga Damascus din.

Share

5 1 vote
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments