Girgizar Kasa A Habasha Mai Karfin Awo 5.8 Da Gargadin Bala’in Da Zai Biyo Baya

Girgizar kasa mai karfin awo 5.8 ta afku a kasar Habasha, kuma labarai sun yi gargadin bala’i mai ban tsoro da zai biyo baya Cibiyar

Girgizar kasa mai karfin awo 5.8 ta afku a kasar Habasha, kuma labarai sun yi gargadin bala’i mai ban tsoro da zai biyo baya

Cibiyar bincike kan yanayin kasa ta kasar Jamus ta watsa rahoton cewa: Girgizar kasa mai karfin awo 5.8 ta afku a kasar Habasha a yau Asabar.

Cibiyar ta bayyana cewa: Girgizar kasar ta afku ce a nisan kilomita 142 a shiyar gabas da birnin Addis Ababa, a zurfin kasa kilomita 10.

Girgizar kasar ta biyo bayan wasu girgizar kasa da suka a afku a kasar ta Habasha a ‘yan kwanakin da suka gabata.

Wannan yanki ya fuskanci girgizar kasa mai karfin awo 5.5 a ranar Juma’ar makon da ya gabata, da kuma wasu jerin girgizar kasa da ba su da karfi fiye da talatin a cikin makonnin baya.

A cikin wannan yanayi, wani masanin ilmin kasa na kasar Masar ya yi gargadin fadada ayyukan aman wuta a kasar Habasha bayan da dutsen Dauphin ya yi a yau, la’akari da cewa girgizar kasar da Habasha ta gani a baya-bayan nan ya sa dutsen ya fashe.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments