An Kashe Mutum Akalla 70 A Yaki Tsakanin HKS Da Yan Tawaye A Kudancin Kasar Siriya

An kashe mutane fiye da 70 a fafatawa tsakanin sojojin Hai’at Tahrin Assham Masu Iko da kasar Siriya ta wata kungiyar yan tawaye a yammacin

An kashe mutane fiye da 70 a fafatawa tsakanin sojojin Hai’at Tahrin Assham Masu Iko da kasar Siriya ta wata kungiyar yan tawaye a yammacin kasar.

Ciobiyar watsa labarai ta SOHR ta bayyana cewa an fara yakin ne bayan da aka kaiwa sojojin HIS harin ba zata a kan bakin teku a daren Jumma.a.

SOHR wacce take sanya ido a kan al-amuran kasar Siriya ta bayyana haka a shafinta na X a safiyar yau Jumma’a. Ta kuma kara da cewa. a bakin ruwan garin Jabbeh kusa da lardin lardin lantaki mutane 48 aka kashe.

Labarin ya bayyana cewa wannan shi ne hari mafi muni a kan sabbin masu iko da kasar Sham tun bayan sun kwace iko da kasar a cikin watan Desemban da ya gabata.

Labarin ya kara da cewa an kashe sojojin HTS akalla 16 a fafatawar jiya Alhamis, a bakin tekun Medeteranian a cikin lardin Lantakiya, inda Alawiyawa da musulmi mabiya mazhabar shia suka fi yawa a kasar.

A wannan yankin ne sansanin sojojin kasar Rasha suke ayyukansu a bakin ruwan Medeteranian. Alawiyawa sun aikwa sakonni a shafin Facebook inda suke bayyana cewa ta yaya, gwamnatin HTS zata yi amfani da hare-haren jiragen yakin helkomta a kansu bayan sun gudanar da zanga-zangar lumana don neman hakkinsu.

Share

5 1 vote
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments