‘Yan Daban Gwamnatin Siriya Sun Kai Farmaki Kan Masallacin ‘Yan Shi’a A Birnin Damascus  

‘Yan daban sabuwar gwamnatin Siriya sun kai samame wani Masallaci da ke cikin karkarar birnin Damascus tare da korar masu ibada Kungiyar kare hakkin bil’adama

‘Yan daban sabuwar gwamnatin Siriya sun kai samame wani Masallaci da ke cikin karkarar birnin Damascus tare da korar masu ibada

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasar Siriya ta sanar da cewa: Jami’an tsaron kasar da ke da alaka da gwamnatin rikon kwarya a kasar Siriya sun kai farmaki kan Masallata da ‘yan kasar ke gudanar da ibadu a cikin masallacin Al-Mustafa da ke unguwar Andalusia a garin Babila a cikin karkarar birnin Damascus, bayan da suka ki mika musu makullan masallacin da kuma rufe Masallacin saboda sabanin Mazhaba.

Hakazalika ‘yan daban Al-Jolani sun lalata ofisoshi da hotuna da ke cikin masallacin, lamarin da ya fusata mazauna birnin.

Masu lura da al’amura sun bayyana cewa: An gina masallacin ne da kudade daga mabiya Ahlul-baiti (amincin Allah ya tabbata a gare su), kuma ba shi da alaka a hukumance da ma’aikatar kula da harkokin Baitul-Malin addini na kasar Siriya, wanda hakan na iya zama dalilin cece-kuce kan gudanar da masallacin.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments