WSJ: Amurka Tana Tara Rundunonin Yaki A Zagayen Kasar Venezuela

Jaridar Wall Street Jouranl ta kasar Amurka ta buga labarin da yake cewa, kasar Amurka ta fara girke makamai a kusa da tekun Caribbean da

Jaridar Wall Street Jouranl ta kasar Amurka ta buga labarin da yake cewa, kasar Amurka ta fara girke makamai a kusa da tekun Caribbean da kuma wasu jiragen sama a arewacin kasar Venezuela.

Labarin ya kara da cewa;Rundunar da ma’aikatar yakin Amurka ta “Pentagon” ta girke ta zaratan mayakan kundunbala ce wacce ta kashe Usama Bin Ladan a kasar Pakistan.

Wani sashe na rundunar ya hada jirage masu saukar Angulu da ake iya amfani da su wajen kai hari.

A cikin kwanakin bayan nan dai Amurka ta kara matsin lamba akan kasar Venezuela ta hanyar kai wa jiragen ruwan da suke fitowa daga kasar hare-hare, bisa zargin cewa suna dauke da muggan kwayoyi zuwa Amurka.

Gwamnatin Venezuela da kasashen yankin masu kin jinin danniyar Amurka sun yi watsi da zargi tare da bayyana shi a matsayin wani sabon  yunkuri na sake dawo da yake-yaken da Amurka ta yi a cikin wannan yankin na Caribbean a shekarun baya.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments