Wakilin Amurka Na Musamman Ya Ziyarci Kasar Sudan Tare Da Ganawa Da Jami’anta

Wakilin Amurka na musamman ya ziyarci Sudan tare da jaddada bukatar Amurka na ganin an kawo karshen yaki a kasar Kimanin watanni 9 da nada

Wakilin Amurka na musamman ya ziyarci Sudan tare da jaddada bukatar Amurka na ganin an kawo karshen yaki a kasar

Kimanin watanni 9 da nada shi a matsayin wakilin Amurka a Sudan, Tom Perriello, ya ziyarci Sudan tare da gudanar da zaman tattaunawa da shugaban Majalisar Gudanar da Mulkin kasar karkashin gwamnatin rikon kwarya Janar Abdul-Fattah Al-Burhan.

Bangarorin biyu sun gudanar da shawarwari ne a birnin Port Sudan a ziyarar jami’in na Amurka ta farko a kasar, Periello ya tattauna da Shugaban Majalisar Gudanar da Mulki, Abdel Fattah al-Burhan da mataimakinsa Malik Agar da Ministan Harkokin Waje Ali Youssef, da shugaban kabilar Masalit, Sa’ad Bahr al-Din, da kuma wakilan kungiyoyin fararen hula da hukumomin Majalisar Dinkin Duniya, inda suka tattauna game da yanayin ayyukan jin kai, neman hanyar dakatar da yaki a kasar, da kuma batun gudanar da tsarin siyasa.

Tun a watan Agustan da ya gabata ne aka shirya Periello zai kai Ziyara zuwa birnin Port Sudan, amma a kan sharadin zai gana da jami’an Sudan ne a filin jirgin saman birnin, saboda abin da aka kira kudurin tabbatar da tsaro saboda rashin ofishin jakadancin Amurka a Sudan, amma majalisar gudanar da mulkin Sudan ta ki amincewa da hakan.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments