Trump Ya Sake Mayar Da Kasar Cuba  Cikin Jerin Masu Tallafawa Ta’addanci  Bayan Da  Joe Shugaban  Ya Cire Ta

Fadar  mulkin Amurka “White House”  ta ba da sanarwan cewa shugaba Donal Trump ya soke cire kasar Cuba daga cikin jerin kasashen da Amurka ta

Fadar  mulkin Amurka “White House”  ta ba da sanarwan cewa shugaba Donal Trump ya soke cire kasar Cuba daga cikin jerin kasashen da Amurka ta dauka a matsayin  masu tallafawa ayyukan ta’addanci.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto majiyar fadar white House a ranar Litinin, tana cewa wannan matakin zai kara rikicin da ke tsakanin kasashen biyu na kimanin shekaru 60 da suka gabata.

Shugaban Biden dai ya yi kokarin sassautawa kasar ta Cuba takunkuman tattalin arziki da kuma matsin lamban da takewa kasar ta cuba tun lokacin yakin cacan baki. Sabon matakin na Shugaba  Trump ya sake mayar da al’amurra baya a alakar kasashen biyu.

A ranar 14 ga watan Janairu ne tsohon shugaban Amurka Joe Biden ya soke dokar sanya Cuba cikin Jerin kasashen wadanda Amurka ta dauka a matsayin masu tallafawa ayyukan ta’addanci.

A ranar da aka rantsar da shi a matsayin shugaban kasa Trump ya soke dokokin tsohuwar gwamnatiun har guda 78.

Kafin haka dai Obama ma ya soke wannan dokar a shekara ta 2015, amma Trump ya sake maida ita, sannan Biden ya soke, yanzu kuma  Trump  din ya sake maida  ita a karo na biyu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments