Sudan: Rundunar Daukin Gaggawa ( R.S.F ) Ta Kashe Mutane 75 A Wani Hari Da Ta Kai Wa Masallaci A Garin Al-Fasha

Tashar talabijin din al-mayadin ta bayar da labarin cewa, rundunar kai daukin gaggawar ta kai hari akan masallacin unguwar “Abu Shauk” dake birnin Al-fasha a

Tashar talabijin din al-mayadin ta bayar da labarin cewa, rundunar kai daukin gaggawar ta kai hari akan masallacin unguwar “Abu Shauk” dake birnin Al-fasha a lokacin sallar asuba.

Da safiyar jiya juma’a ne dai mayakan rundunar ta r.s.f su ka kai wa masallacin na Abu Shauka hari a birnin al-fasha da shi ne babban birnin gundunar Darfur ta Arewa.

Mutane 75 ne su ka yi shahada sanadiyyar wannan harin da aka bayyana a matsayin kisan kiyashi.

Wata majiya a garin da aka kai wa harin, ta ambaci cewa wadanda suke salla a masallacin ‘yan hijira ne da aka koro daga yankunan da yaki ya yi tsanani.

Kwamitin da yake kula da kungiyoyin dake fada da rundunar rsf ya ce; An yi amfani da jirgin sama maras matuki ne wajen kai wa masallacin hari.

A baya kwamitin bincike na MDD ya zargi rundunar kai daukin ggagawa da tafka laifi akan bil’adama. Ta kuma zargi rundunar da cewa yana hana mutane samun abinci,kuma tana lalata asibitoci.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments