Rikici Yana Ci Gaba Da Gudanar A Kasar Sudan Tsakanin Sojoji Da Dakarun Kai Daukin Gaggawa

Rikici tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na kasar yana ci gaba da habaka a wurare da dama na kasar Kasar Sudan dai

Rikici tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na kasar yana ci gaba da habaka a wurare da dama na kasar

Kasar Sudan dai na fuskantar tabarbarewar harkokin tsaro cikin hanzari, a daidai lokacin da ake ci gaba da gwabza fada tsakanin sojoji da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces (RSF), a cikin sarkakkiyar yanayin jin kai da na siyasa da kuma fadadan rikici a jihohi daban-daban.

Fadace-fadace a Sudan suna ci gaba da karuwa, inda ake ci gaba da gwabza fada tsakanin sojoji da mayakan kungiyar Rapid Support Forces, inda sojojin saman Sudan suka zafafa kai hare-hare ta sama ta hanyar amfani da jiragen sama marasa matuka ciki, kuma suka yi luguden wuta kan wasu muhimman wurare na kungiyar Rapid Support Forces a jihar Kordofan ta Arewa.

Hare-haren sun fi tsanani ne a yankin Kilo Zero dake arewacin Bara da Ummu Sayala, tare da lalata motocin soji da kayayyakin aiki, baya ga hasarar dimbin dakarun kungiyar Rapid Support Forces, kamar yadda majiyoyi da dama suka tabbatar da nasarar sojojin Sudan kan ‘yan tawaye.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments