Najeriya: Matatar Dangote Za Ta Mika Tataccen Mai Lita Biliyan 1.5 A Watan Disamba

Matatar Man Fetur ta Dangote a Najeriya ta sanar a wannan  Litinin cewa tana da ikon isar da lita biliyan 1.5 na man fetur a

Matatar Man Fetur ta Dangote a Najeriya ta sanar a wannan  Litinin cewa tana da ikon isar da lita biliyan 1.5 na man fetur a kowane wata, kuma ta yi kira ga hukumar kula da masana’antu da ta tabbatar da hakan a cikin alkalumanta na yau da kullun, bayan da hukumar ta fitar da bayanai da ke nuna cewa matatar tana samar da kusan kashi daya bisa uku ne kawai na wannan adadi.

Ikirarin da ake yi cewa matatun man fetur na Najeriya ba su iya biyan bukatun kasa ba wani bangare ne na dalilin da ya sa gwamnati ta yi watsi da shirinta na hana shigo da kayayyakin man fetur da aka tace a watan da ya gabata ba.

Matatar ta kiyasta bukatar da ake da ita a Najeriya da cewa ya kai kusan lita miliyan 55 a kowace rana, wato kimanin lita biliyan 1.67 a kowane wata.

Matatar Dangote ta ce a shirye take ta samar da wannan adadi, kuma za ta iya yin hakan, inda a yanzu za ta iya samar da lita biliyan 1.5 na man fetur a kowane wata daga wanann watan Disamba da Janairu, inda kuma za ta kara adadin zuwa lita biliyan 1.7 a kowane wata daga watan Fabrairun 2026 zuwa gaba.

Matatar ta kuma bukaci Hukumar Kula da Man Fetur da Iskar Gas ta Jihar New Mexico (NOG) da ta tallafa wa ayyukanta ta hanyar barin shigo da danyen mai, da sauran kayayyakin da take bukata ba tare da wani cikas ba.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments