Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Kasar Siriya Tana Kara Shiga Cikin Halin Tsaka Mai Wuya

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Kasar Siriya na cikin mawuyacin hali na gwaji Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Kasar Siriya na cikin mawuyacin hali na gwaji

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana cewa: Shakka babu duniyar musulmi ta damu matuka kan makomar yankin yammacin Asiya, bisa la’akari da yanayin da ake ciki a kasashen Siriya da Falastinu.

Araqchi ya rubuta a cikin wata makala da aka buga a jaridar Al-Akhbar ta kasar Lebanon cewa: Siriya a yau tana cikin gwaji mai wahala. Sannan akwai barazanar da ke tattare da yunkurin kungiyoyin ta’addanci irinsu Al-Qaeda da ISIS, kuma hakan ya kara dagula al’amura a yankin.

Al’ummar wannan yanki suna da muhimmiyar rawar da zasu taka wajen tsara makomar siyasar duniyar Musulunci, domin kuwa a cikin shekaru aru-aru an fuskancin ire-iren wadannan matsaloli kuma an samu nasarar magance su, kamar yadda a wasu shekaru masu yawa aka fuskanci munanan hare-hare da ya biyo bayan rikicin Yahudawa da Kiristanci na Turai, wanda ya bazu zuwa yankin nan bayan yakin duniya na biyu, musamman saboda rashin mutunta hakkin al’ummar wannan yanki.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments