MDD: Isra’ila Na AmfaniDa Hanyoyin Da Suka Yi Daidai Da Kisan Kare Dangi A Gaza

Hanyoyin yakin Isra’ila a Gaza sun yi daidai da kisan ƙare dangi, ciki har da fararen hula wadanda aka kashe tare da azabtar da Falasdinawa

Hanyoyin yakin Isra’ila a Gaza sun yi daidai da kisan ƙare dangi, ciki har da fararen hula wadanda aka kashe tare da azabtar da Falasdinawa da gangan, a cewar wani Kwamitin Majalisar Dinkin Duniya na Musamman.

Harin bama-bamai da Isra’ila ta kai a unguwar Sheikh Radwan da ke birnin Gaza inda fararen hula ke zaune, ya kashe Falasdinawa akalla uku.

A wani hari na daban da aka kai a wajen makarantar Hamama, Isra’ila ta raunata Falasdinawa 10, in ji cibiyar yada labarai ta Falasdinu (PIC).

Har ila yau Isra’ila ta tsananta kai hare-hare a duk fadin Gaza, inda aka harba makaman atilari a yankunan kudanci da gabashin unguwar Zeitoun.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments