Kungiyar Hizbullah Ta Lebanon Ta Janyo Mummunar Hasara Ga Yahudawan Sahayoniyya

Majiyoyin Turai sun bayyana cewa: Martanin baya-bayan nan na kungiyar Hizbullah ya haifar da hasarar rayuka da jikkata da dama a haramtacciyar kasar Isra’ila Majiyoyin

Majiyoyin Turai sun bayyana cewa: Martanin baya-bayan nan na kungiyar Hizbullah ya haifar da hasarar rayuka da jikkata da dama a haramtacciyar kasar Isra’ila

Majiyoyin tsaron Turai sun bayyanawa tashar talabijin ta Al-Mayadeen cewa: Hare-haren da kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullahi ta kaddamar kan sashi na 8200 a Glilot da kuma sansanin Ein Shemer sun janyo munanan hasarori ga haramtacciyar kasar Isra’ila.

Majiyoyin sun tabbatar da cewa: Hare-haren sun yi sanadiyyar halakar da dama da kuma jikkata musamman a sashin leken asirin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila na sashin mai lamba 8200, wanda wadanda suka jikkata suka kai yahudawan sahayoniyya 74.

Majiyoyin sun kara da cewa: Adadin wadanda suka mutu a Glilot da Ein Shemer ya kai yahudawa 22, kuma wadanda suka jikkata sun haura 70.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments