Kotun Kasa Da Kasa Zata Fitar Da Sammacin kama Masu Hannu A Aikata Muggan Laifuka A Darfur Na Sudan

Kotun da ke shari’ar manyan laifuka a duniya tana gab da fitar da sammacin neman kama wadanda suka aikata muggan laifukan Darfur na kasar Sudan

Kotun da ke shari’ar manyan laifuka a duniya tana gab da fitar da sammacin neman kama wadanda suka aikata muggan laifukan Darfur na kasar Sudan

Mai gabatar da kara na kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, Karim Khan, ya sanar da cewa ofishinsa zai bukaci fitar da sammacin kama wadanda ake zargi da aikata ta’asa a yankin yammacin Darfur na kasar Sudan nan kusa kadan.

Karim Khan ya bayyana wa Kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya cewa: Ana aikata muggan laifuka a yankin Darfur da ke yammacin kasar Sudan a lokacin da muke magana kan halin yankin da kuma kullum rana a matsayin makamin yaki a kasar.

Khan ya kara da cewa hakan ya samo asali ne sakamakon bincike da aka gudanar a tsanake bisa hujjoji da bayanan da ofishinsa ya tattara.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments