Shugaban kasar Afirka Ta kudu Cyril Ramaphosa da ya gabatar da jawabi a taron babban zauren MDD ya jaddada matsayar kasarsa na son ganin an bai wa al’ummar Falasdinu kasarsu akan iyakar 1967.
Da yake Magana akan abinda yake faruwa yanzu a Gaza, shugaban kasar ta Afirka Ta Kudu ta caccaki HKI akan yadda take azabatar da al’ummar Falasdinu a dunkule.
Haka nan kuma ya yi kira da a kawar da dukkanin abubuwan da suke kawo cikas wajen kafawa Falasdinawan kasar tasu.