Jiragen Yakin HKI Sun Yi Luguden Wuta Kan Garin Lantakia Na Kasar Siriya

Tun bayan faduwar gwamnatin Bashar Al-Asad na kasar Siriya ne, sojojin HKI suka fara kai hare-haren don lalata makaman kasar ta Siriya a wurare daban

Tun bayan faduwar gwamnatin Bashar Al-Asad na kasar Siriya ne, sojojin HKI suka fara kai hare-haren don lalata makaman kasar ta Siriya a wurare daban daban a kasar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bada labarin cewa, a jiya Asabar ma, jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan rumbunan ajiyar makamai a birnin Lantakia na kasar ta Sirya.

Mazauna yankin sun bayyana cewa sun ji karar fashe-fashe makamai a gewajen garin, sannan kamfanin dillancin labaran Sputnic na kasar Rasha suma sun tabbatar da cewa an ji karar fashe-fashe a birnin, kuma jiragen yakin HKI ne suka kai hare hare.

Har yanzun babu labarin irin asarorin da aka yi sanadiyyar hare-haren na HKI a Lantakia.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments