Jakadan Iran Ya Bankado Daya Daga Cikin Sharuddan Da Amurka Ta Gindaya Wa Sabbin Mahukuntan Siriya

Amurka ta gindaya sharudda ga sabuwar gwamnatin Siriya kafin tallafa mata don samu damar gudanar da shugabanci a kasar Jakadan Iran a kasar Lebanon Mojtaba

Amurka ta gindaya sharudda ga sabuwar gwamnatin Siriya kafin tallafa mata don samu damar gudanar da shugabanci a kasar

Jakadan Iran a kasar Lebanon Mojtaba Amani ya rubuta wani sako a dandalin “X” da a ciki ya tabo batun sharuddan da Amurka ta gindaya wa sabuwar gwamnatin Siriya kafin samun goyon bayanta.

A cikin sakon nasa, Amani ya bayyana wasu daga cikin sharuddan da Amurka ta gindaya kafin goyon bayan sabbin mahukuntan kasar Siriya, inda ya ce: Bayan ganawar da wakilin Amurka ya yi da Al-Julani jagoran ‘yan adawar da suka kifar dagwamnatin Siriya, Amurka ta bayyana cewa: Dole ne sabuwar gwamnatin Siriya ba za ta bai wa Iran wani matsayi ba domin samun kyakkyawar alaka da gwamnatin kasar ta Siriya.

Amani ya kara da cewa: Shi shaida ne cewa a shekara ta 2011 zuwa 2013 Amurka ta dage kan gindaya irin wannan sharudda ga kungiyar ‘yan uwa musulmi ta Ihwanul-Muslimina, kuma sun gindaya wa Muhammad Morsi, (Allah Ya yi masa rahama) irin wannan sharudda, kuma bayan sun samu damar ganawa da Morsi shi kadai, sun jaddada masa wannan sharudda amma a lokacin da suka ga ya yi watsi da sharuddan. Sai suka zarge shi da cin amanar Amurka kuma suka goyi bayan abin da ya faru gare shi.

Share

4 1 vote
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments