Jakadan Iran A Lebanon: Amurka Ta kafawa Sabuwar Gwamnatin Syria Sharadin Kin Amincewa Da Iran

Jakadan jamhuriyar musulunci ta Iran a kasar Lebanon Mujtaba Amani ya ne ya bayyana hana a wani rubutu da ya yi a shafinsa na hanyar

Jakadan jamhuriyar musulunci ta Iran a kasar Lebanon Mujtaba Amani ya ne ya bayyana hana a wani rubutu da ya yi a shafinsa na hanyar sadarwa ta al’umma.

Mujtaba Amani ya waffala a shafinsa na X cewa:

“Tawagar Amurka da ta gana da Julani , ta kafa wa sabuwar gwamnatin Syria sharadin cewa; kar ta kuskura ta bai wa Iran damar taka kowace irin rawa a cikin Syria,idan har  tana son alakarsu ta yi kyau da Amurkan.

Bugu da kari ya ce:  Na kasance shaida akan wannan irin  nasihar da Amurkan ta kafawa  Ikhwanul-Muslimi a tsakanin 2011 zuwa 2013; sun kuma kafawa Muhammadu Mursi Allah ya yi masa rahama, irin wannan sharadin. Da su ka tabbatar da cewa Mursi ya zama shi kadai, ( babu wata kasa mai taimaka masa kamar Iran) sai su ka ci amanarsa kamar yadda su ka saba; abinda ya faru ( juyin mulkin Sisi) ya faru.”

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments