Isra’ila ta Kai Jerin hare-hare Kan Cibiyoyin yemen Ciki Har Filin Jirgin Sanaa

Bayanai daga Yemen na cewa jiragen Yakin Isra’ila sun kai hari a filin jirgin saman Sanaa da wasu wuraren da ‘yan Houthi ke rike da

Bayanai daga Yemen na cewa jiragen Yakin Isra’ila sun kai hari a filin jirgin saman Sanaa da wasu wuraren da ‘yan Houthi ke rike da su.

An kai hare-hare ta sama a wurare da dama a kasar Yemen a ranar Alhamis din ann, ciki har da filin tashi da saukar jiragen sama na kasa da kasa na Sanaa da wata cibiyar samar da wutar lantarki, a cewar shaidu da kuma masu tayar da kayar baya.

Tashar talabijin ta Al-Masirah ta rawaito hare-harenna  Isra’ila.”

A nata bangaren, Isra’ila, ta tabbatar da kai hare-haren kan abinda ta danganta da “makamai na soji” na Houthis.

Hare-haren dai na zuwa ne bayan wani sabon harin makami mai linzami da aka kai kan Isra’ila a makon jiya, wanda ‘yan Houthi suka yi ikirarin cewa na goyan bayan al’ummar Gaza ne da Isra’ila ke zalinta.

Tun lokacin da aka fara yakin Zirin Gaza a ranar 7 ga watan Oktoban 2023, ‘yan Houthis sun kaddamar da hare-hare da dama kan Isra’ila, suna masu ikirarin goyan bayan Falasdinawa.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments