Adai dai lokacin da bikin cika shekaru 55 na kulla hulda diplomsiya tsakanin Iran da China ke kara karatowa ta , dukkan kasashen biyu suna kokarin ganin sun kara karfafa alakar dake tsakaninsu , Ambasado Ahmad Fazli ya jaddada game da muhimmancin karfafa dangantaka a mataki na kasa da kasa, bisa hangen nesa da girmama juna.
Ganawar da aka yi tsakanin jakadan kasar iran a bejin Rahmani Fazli da Miao Deyu matakimakin ministan harkokin wajen kasar china ta nuna aniyar kasashen biyu na kara karfafa dangantakarsu ta dogon lokaci.
A lokacin ganawar da mataimakin ministan harkokin wajen kasar china rahmani ya jadda muhimmancin kara dankon zumunci tsakanin iran da china, musamman ma yin muhimmacin aiki tare a yankin, don haka bikin cika shekara 55 zai zama wata damace da zaa kara fadada dangantaka da yin aiki tare
Bangaren iran a shirye yake yayi aiki da kasar china don karfafa muamala da zurfafa yin aiki tare a bangarori daban daban bisa yarjejeniyar da shuwagabannin kasashen biyu suka cimma matsaya akai,