HKI tana ci gaba da kai wa muhimman cibiyoyi da gidajen Falasdinawa a fadin Gaza.
Majiyar Falasdinawa ta ce daga safiyar yau Laraba adadin wadanda su ka yi shahadar sun kai 45 sanadiyyar hare-haren da jiragen yakin ‘yan sahayoniyar su ka kai.
Har ila yau an sami wasu Karin shahidan biyar a wuraren karbar agaji dake arewacin Rafaha.
A wani labarin mai alaka da hakan shugaban hukumar lafiya ta duniya ( w.h.o) Tedross Adhanom ya ce; Kai hare-haren da ake yi a kusa da asibitin Rantisy, dake Gaza, ya yi sanadiyyar tsayuwar aikin Asibiti, domin rashin tsaro.
Har ila yau ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta kara da cewa; Jinkirin shigar da makamashi zuwa yankin yana barazanar tsayar da aikin injinan da suke bayar da wuta a asibitin idanu,wanda yake yi wa mutane da dama aiki.
Ofishin hukuma a Gaza ya sanar da cewa, mutanen da sun kai 900,000 sun fice daga gidajensu amma kuma suna ci gaba da riko da ci gaba da zamansu a cikin kasarsu.
Bugu da kari, ‘yan mamayar suna ci gaba da tilastawa mutanen na Gaza ficewa daga gidajensu, zuwa yankunan kudancin Gaza, ta hanyar kai musu hare-hare.
Haka nan kuma da akwai wasu Karin mutanen 334,000 da aka fitarsa fita daga gidajensu a cikin kwanaki uku, da hakan ya sa yawansu ya kai 60,000.