Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci A Iran Da Sojojin Kasa Azarbaijan Sun Fara Atisayen  Hadin Giwa A Kan Iyakokin Kasashen Biyu

Dakaru na musamman daga rundunar kare juyin juya halin musulunci (IRGC) a nan Iran da kuma sojojin kasar Azairbaijan sun fara atisayen hadin giwa a

Dakaru na musamman daga rundunar kare juyin juya halin musulunci (IRGC) a nan Iran da kuma sojojin kasar Azairbaijan sun fara atisayen hadin giwa a tsakaninsu a jiya Lahadi.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar IRGC na cewa atisayen zai dauki kwanaki 4 cur ana gudanarwa. Sannan manufar sa itace ce karfafa harkokin tsaro a kan iyakar kasashen biyu, musamman a bangaren yaki da yan ta’adda da kuma musayar dabarbarun yaki.

Kafin haka dai kasashen biyu, musulmi sun kulla yarjeniyar tsaro a tsakaninsu, wanda ya basu damar aiki tare da kuma bunkasa harkokin tsaro a tsakanin kasashen biyu.

Atisayen wanda aka sanyawa suna ‘Gamayyar Aras’ zai taimakawa kasashen biyu sabawa da yanayin kan iyakar kasashen biyu

Wannan dai shi ne atisayen soje mafi girma a tsakanin kasashen biyu sannan kuma ana gudanar da shi ne a lardin Ardabil na kasar Iran wanda kuma yake kan iyakar kasashen biyu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments