Aragchi Yace Duk Wani Harin Da Aka Kaiwa Cibiyoyin Nukliyar Kasar Iran Hakan Wata Musiba ce Ga Yankin Asiya Ta Yamma

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa duk wani hari kan daya daga cikin cibiyoyin Nukliyar kasar Iran daga HKI ko Amerika,

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa duk wani hari kan daya daga cikin cibiyoyin Nukliyar kasar Iran daga HKI ko Amerika, wannan wata musiba ce da yankin, kuma wadanda suka kai harin zasu gamu da maida martani ba tare da jinkiri ba.

Tashar talabijin ta Presstva nan Tehran ta nakalto Abbas Aragchi yana fadar haka a wata hirar da ta hada shi da tashar talabijin ta Sky News a nan Tehran.

Ya kuma kara da cewa, ban tsamman zasu yi haka ba. Amma idan sun, to kuwa ba zasu ji ta da dadi ba.

Yace: JMI ta rattaba hannu a kan yarjeniyar Nukliya da manya-manyan kasashe 6 a duniya kan shirin ta na makacin Nukliya wanda ake fi sani da JCPOA amma a shekara ta 2018 shugaba Trump a wa’adin mulkinsa na farko ya fitar da Amurka cikin yarjeniyar, sannan ya dora mata takunkuman arziki mafi muni a tarihin kasar Iran, da nufin karya gwamnatin JMI. Amma hakan bai faru ba. Sai kuma a shekara ta 2019 Iran ta fara dauke kataita shirin makamashin nukliyarta ta zaman lafiya da ta saboda maida martani ga dayan bangaren wacce ta sabawa alkawulanta su.

A baya-bayan nan mun ji Trump yana fadin wasu maganganu, wanda yake cewa masu dadi, amma sai mun ganshi a kasa. Sai dai yakamata Amurka da kawayenta su sani ka cewa Iran ba zata sake tattaunawa da su da sauki ba.

Daga karshe ministan ya mayarwa Trump Martani kan mutanen gaza, da cewa ya maida HKI zuwa Green Island ya fi mata sauki da ya maida Falasdinawa Masar da Jordan.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments